Kotu a Masar ta wanke Hosni Mubarak
Wata kotu a Masar ta yi watsi da tuhume-tuhumen da ake yi wa
tsohon Shugaban kasar Hosni Mubarak, a kan daya daga cikin laifukan da ake
zarginsa da su na cin hanci.
Lauyan Mista Mubarak ya ce nan ba da jimawa ba za a saki tsohon shugaban
kasar, idan har aka wanke shi daga daya daga cikin tuhumar da ake masa.A cewarsa, zargin cin hanci da rashawa ne kawai ya sa ake ci gaba da tsare Mista Mubarak.
Sai dai har yanzu akwai wata shari'ar da zai kara fuskanta a kan hannun wajen kashe masu zanga-zanga lokacin boren da ya hambarar da shi daga kan mulki a shekarar 2011.
No comments:
Post a Comment